Isa ga babban shafi
Faransa

'Yan takara sun fara Muhawara a zaben Faransa

A yau ne litinin 'yan takara biyar daga cikin 11 da ke neman kujerar shugabancin Faransa, za su tafka muhawara ta farko a talabijin. Muhawarar dake zuwa a dai dai lokacin da hankulan yan kasar ya rabu gani ta yadda wasu daga cikin 'yan takara sunayen su ke gaban alkalan kotu.

'Yan takara a zaben Shugabancin Faransa
'Yan takara a zaben Shugabancin Faransa
Talla

Daga cikin ‘yan takarar da za su shiga wannan muhawara ta farko sun hada da Emmanuel Macron, Francois Fillon,Marine Le Pen, Benoit Hamon da kuma Jean-Luc Melenchon.

Manazarta siyasar Faransa na ganin dan  takara Francois Fillon daga babbar jam’iyyar adawa wanda aka kuma bayyana cewa zai sha kaye tun a zagayen farko na zaben da za a yi a ranar 23 ga watan gobe.

Wasu sun maida hankali kan irin wainar da ake toyawa kama da tanttance 'yan takara a Zaben fitar da gwani, zuwa gwagwarmayar neman goyan bayan 'yan kasar duk da tonon silili da ake ci gaba da samu dangane da wasu 'yan takara a wannan zabe.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.