'Yan takara sun fara Muhawara a zaben Faransa
A yau ne litinin 'yan takara biyar daga cikin 11 da ke neman kujerar shugabancin Faransa, za su tafka muhawara ta farko a talabijin. Muhawarar dake zuwa a dai dai lokacin da hankulan yan kasar ya rabu gani ta yadda wasu daga cikin 'yan takara sunayen su ke gaban alkalan kotu.
Wallafawa ranar:
Daga cikin ‘yan takarar da za su shiga wannan muhawara ta farko sun hada da Emmanuel Macron, Francois Fillon,Marine Le Pen, Benoit Hamon da kuma Jean-Luc Melenchon.
Manazarta siyasar Faransa na ganin dan takara Francois Fillon daga babbar jam’iyyar adawa wanda aka kuma bayyana cewa zai sha kaye tun a zagayen farko na zaben da za a yi a ranar 23 ga watan gobe.
Wasu sun maida hankali kan irin wainar da ake toyawa kama da tanttance 'yan takara a Zaben fitar da gwani, zuwa gwagwarmayar neman goyan bayan 'yan kasar duk da tonon silili da ake ci gaba da samu dangane da wasu 'yan takara a wannan zabe.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu