Dan bindiga ya bude wuta kusa da Masallaci a Faransa
Wani dan bindiga ya buda wuta tare da raunata mutane 8 a kofar wani masallaci da ke garin Avignon da ke kudancin Faransa, al’amarin da mai shigar da kara na gwamnati ya nisanta da ayyukan ta’addanci.
Wallafawa ranar:
‘Yan sanda sun ce da misalin karfe 10 da rabi na daren jiya ne wasu mutane biyu cikin wata mota suka buda wuta a kofar masallacin, inda yanzu haka ake ci gaba da farautar maharan.
Harin na zuwa kwanaki bayan wani mutum ya abka wa masu ibadah a masallacin Cretail kudancin Paris a ranar Alhamis.
Al’ummar musulmi a Faransa sun bayyana damuwa akan yadda ake kokarin kai masu hari a wajen ibadah inda suka yi kira ga mahunkunta wajen tabbatar da tsaro musamman a masallatai.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu