Isa ga babban shafi
Korea ta Arewa

Amurka ta sanyawa kamfanonin Rasha da China takunkumi

KASAR Amurka ta sanyawa wasu kamfanonin kasashen Rasha da China 16 takunkumi saboda abinda ta kira goyan bayan shirin nukiliyar kasar Koriya ta Arewa. Takunkumin na daga cikin matakan da Amurka ke dauka na dakile samun kudade ga Koriyar domin ci gaba da gina makamin.

A baya-bayan nan ne dai shugaban na Amurka ya yabawa Kim Jun-Un kan matakin daya dauke na dakatar da shirin harba wani makami mai linzami zuwa yankin Guam na Amurka
A baya-bayan nan ne dai shugaban na Amurka ya yabawa Kim Jun-Un kan matakin daya dauke na dakatar da shirin harba wani makami mai linzami zuwa yankin Guam na Amurka Reuters
Talla

Sakataren Baitulmalin Amurka, Steven Mnuchin ya ce abin takaici ne ga mutane ko kuma kamfanonin da ke China da Rasha ko kuma wata kasa dabam su taimaka Koriya ta Arewa domin samun kudin da zata ci gaba da gina makaman kare dangi ko kuma hana zaman lafiya.

Takunkumin ya shafi kamfanonin da ke mu’amala da kwal da wasu ma’adinai da kuma hada hadar kudade da kasar ta Koriya.

Matakin dai ya biyo bayan cacar bakin da aka samu tsakanin shugaba Donald Trump na Amurka da takwaransa na Korea ta arewa Kim Jong-un bayan gwajin makami mai linzamin da Koriya ta gudanar.

Shugaba Trump ya bukaci taimakon kasar China domin ganin ta janyo hankalin Koriya tayi watsi da matakan da take dauka.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.