Isa ga babban shafi
Faransa

Ana zargin Faransa da sakaci kan haƙƙin bil'adama

Ƙungiyar kare haƙƙin bil’adama ta Human Rights Watch ta zargi shugaban Faransa Emmanuel Macron da yin riƙon-sakainar-kashi ga kare haƙƙin bil’adama, musamman a kan abinda ya jiɓanci ƴan gudun hijira da kuma cin zarafin bil’adama a ƙasar China.

Shugaban Faransa Emmanuel Macron.
Shugaban Faransa Emmanuel Macron. REUTERS/Francois Mori
Talla

Roth ya ce Macron ya bayar da fifiko a ɓangaren kasuwanci da yaƙi da ta’addanci a kan kare haƙƙin bil’adama.

A lokacin da yake tsokaci bayan fitar da rahoton ƙungiyar na shekara ta 2018, shugabanta Kenneth Roth ya zargi Macron da fuska-biyu a ɓangaren yaki da take hakkin bil’adama.

Ya ƙara da cewa yayin da shugaban na Faransa ke kokawa kan rufdugun da Rasha da Turkiyya ke yi a kan ƴan tawaye na ƙasar Syria, a gefe guda ya kawar da kansa a kan cin zarafin bil’adama da ke faruwa a China, da Masar da kuma jamhuriyar Demokradiyyar Congo.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.