Faransa
Hukumomin Faransa na bukatar gurfanar da Sarkozy gaban kotu
Hukumomi Kasar Faransa sun bukaci gurfanar da tsohon shugaban kasar Nicolas Sarkozy a gaban kotu saboda tuhumar da ake masa na cin hanci da rashawa da kuma kokarin hana alkali gudanar da ayyukan sa.
Wallafawa ranar:
Talla
Mai gabatar da kara ya kuma bukaci lauyan tsohon shugaban Thierry Herzog da wani tsohon mai shari’a Gilbert Azibert da suma su gurfana a gaban kotu akan shari’ar saboda hannun da suke da shi.
Wannan mataki dai ba karamar koma baya bane ga Sarkozy wanda yayi kokarin sake dawowa mulki a watan Nuwambar shekarar 2016 amma bai samu nasara ba.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu