Isa ga babban shafi
Hijira-Turai

Kasa da kashi 5 na 'yan gudun hijira ne kadai ke samun matsugunai - MDD

Majalisar Dinkin Duniya ta ce kasa da kashi 5 na baki 'Yan gudun hijira ne suka samu matsugunai a kasashen Yammacin duniya a shekarar 2018, sakamakon matakin da Amurka ta dauka na rufe kofofin ta wajen karbar irin wadanan mutane.

Wasu tawagar 'yan gudun hijira kenan da ke tattaki akan hanyarsu ta shiga Amurka
Wasu tawagar 'yan gudun hijira kenan da ke tattaki akan hanyarsu ta shiga Amurka REUTERS/Darrin Zammit Lupi
Talla

Hukumar kula da Yan gudun hijira ta Majalisar ta ce Amurka ta karbi baki dubu 17,113 bara, matakin da ya sanya ta a sahun gaba, yayin da wasu kasashe 27 suka karbi baki dubu 55,692 a karkashin shirin hukumar.

Sai dai alkaluman da Amurkar ta karba ya gaza dubu 24,559 da ta karba a shekarar 2017, yayin da a shekarar 2016 kasar ta karbi baki 78,761.

Kasar Canada ce kasa ta biyu da tafi karbar baki, inda a bara ta karbi dubu 7,713 sai kuma Birtaniya a matsayi ta 3 da dubu 5,702 sai kuma Faransa a matsayin na 4 da dubu 5,109.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.