Isa ga babban shafi
Faransa

'Yan sanda sun gargadi Macron kan yawaitar tashin hankali a Faransa

‘Yan Sanda a Faransa sun gargadi shugaba Emmanuel Macron akan karuwar tashe tashen hankalun da ake gani a titunan kasar a daidai lokacin da ya ziyarci wasu wuraren da matsalar tafi kamari saboda munin lamarin.

Shugaban Faransa Emmanuel Macron.
Shugaban Faransa Emmanuel Macron. Guillaume HORCAJUELO POOL/AFP
Talla

Tashe tashen hankulan da ake samu a 'yan kwanakin nan sun jefa matukar fargaba a zukatan jama'a, abinda ya zama batun cece kuce a fagen siyasar kasar ganin cewa a shekara mai zuwa za a gudanar da zaben shugaban kasa.

An zagaya da shugaban unguwanni marasa karfi a cikin motar 'yan sanda inda ya ganewa idanun sa inda ake hada hadar kwayoyi.

Batun tsaro ya zama abinda ya mamaye fagen siyasar Faransa yanzu haka.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.