Isa ga babban shafi
Tarayyar Turai-Covid

Turai na tunanin tilasta wa al'umarta karbar rigakafin Korona

Shugabar Kungiyar Kasashen Turai Ursula von der Leyen ta ce lokaci ya yi da za su yi tunanin tilastawa jama’ar dake yankin karbar maganin rigakafin cutar korona, ganin yadda nau’in Omicron ke saurin yaduwa kamar wutar daji.

 Ursula von der Leyen, shugabar kungiyar Tarayyar Turai.
Ursula von der Leyen, shugabar kungiyar Tarayyar Turai. AFP - KENZO TRIBOUILLARD
Talla

Ganin yadda wasu kasashe suka fara daukar matakai daban daban na dakile cutar, von der Leyen tace duk da yake gwamnatoci ne ke da hurumin tilasta karbar rigakafin, lokaci yayi da ya dace ayi tunani akai.

Tuni Austria ta ce za ta tilasta wa kowa karbar rigakafin nan da watan Fabarariru mai zuwa, yayin da Jamus ke tunani akai.

Karuwar masu kamuwa da cutar covid-19 ya sa wasu gwamnatoci a nahiyar Turai suka maido da dokar tilasta sanya mayanin fuska, matakan bayar da tazara da kuma talaita zirga-zirga a kokarin da suke na rage yaduwar cutar, a yayin da masu sana’o’i ke fargabar samun maimaicin abin da ya faru a lokacin Kiristimeti na shekarar da ta gabata.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.