Isa ga babban shafi

Halin da mutane ke ciki a gabashin Ukraine na da matukar tayar da hankali - MDD

Majalisar Dinkin Duniya ta ce halin da ake ciki a gabashin Ukraine, musamman dangane da ayyukan jin kai, yana da matukar tayar da hankali, tare da gargadin cewa lamurra na kara kazancewa watanni hudu bayan mamaye kasar da Rasha ta yi.

Wasu 'yan kasar Ukraine da yaki ya lalata muhallansu.
Wasu 'yan kasar Ukraine da yaki ya lalata muhallansu. © REUTERS/Alexander Ermochenko
Talla

Sanarwar hukumar kula da ayyukan jinkai ta majalisar dinkin duniya OCHA ta ce al’amura sun fi kazancewa a Donbas da kuma Severodonetsk dake gabashin Ukraine.

Daruruwan fararen hula ake kyautata zaton sun makale a birnin na Severodonetsk, inda ake sa ran wasunsu sun samu fakewa a masana'antar sinadarai ta yankin.

Majalisar Dinkin Duniya ta ce ana samun raguwar samun ruwa mai tsafta, abinci, tsaftar muhalli da wutar lantarki a birnin, matsalolin da suka yi mummunar illa ga fararen hula, ciki har da ma'aikatan agaji.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.