Schalke 04 na neman Moses na Najeriya
Kungiyar Kwallon kafa ta Schalke 04 da ke buga gasar Bundesliga ta Jamus, ta shiga cikin jerin manyan kungiyoyin Turai da ke neman kulla kwantiragi da Victor Moses na Najeriya a daidai lokacin da ake ci gaba da cefanen 'yan wasa a wannan wata na Janairu.
Wallafawa ranar:
Rahotanni na cewa, Schalke 04 na burin sayen Moses ne daga Chelsea domin taimaka ma ta a fafutukarta ta tsallake karewa a matakin ‘yan dagaji.
Akwai kungiyoyi irin su Fulham da Crystal Palace na Ingila har ma da Fernabache ta Turkiya da ke neman kulla kwantiragi da dan wasan.
Bisa dukkan alamu, Fernabache ta fi nuna cewa, a shirye take ta sauke kudaden saye da kuma biyan tsohon dan wasan na Najeriya.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu