Isa ga babban shafi

Macron ya kaddamar da kidayar kwanakin gasar Olympics ta Paris 2024

Shugaban Faransa Emmanuel Macron ya kaddamar da kidayar kwanakin fara gudanar babbar gasar Olympic ta Paris 2024 a daidai lokacin da hukumomin kasar ke rige-rigen inganta fasalin hanyoyin sufuri na birnin Paris. 

Shugaban Faransa, Emmanuel Macron da magajiyar garin birnin Paris Anne Hidalgo a wajen gangamin sanarwar gasar Olympics ta 2024 a watan Yunin 2017.
Shugaban Faransa, Emmanuel Macron da magajiyar garin birnin Paris Anne Hidalgo a wajen gangamin sanarwar gasar Olympics ta 2024 a watan Yunin 2017. Reuters/Jean-Paul Pelissier
Talla

Mahukuntan Paris na Faransa na son gudanar da gagarumin bikin da ba a taba ganin irinsa ba na bude babbar gasar ta Olympic, yayin da shugaba Macron ya karbi bakwanci masu shirya gasar da ‘yan kasuwa a fadarsa ta Elysee domin tattaunawa game da shirye-shiryen gudanar da ita. 

Shugaba Macron ya kuma  yi wa daruruwan ma’aikatan gwamnati masu ruwa da tsaki jawabi a shalkwatan jami’an ‘yan sandan Paris da ke kusa da gabar kogin Seine duk dai karkashin shirye-shiryen karbar bakwancin gasar ta Olympic. 

Shugaba Macron ya kuma yi tsokaci kan aikin tsaftace kogin Seine wanda ya gurbace soasai a daidai lokacin da ya rage kwanaki 500 a fara gasar ta Olympic. 

Mutanen birnin Paris sun jima suna fatan a gyara wannan kogin ta yadda za a ci gaba da yin iyo a cikinsa, inda har a 1988, tsohon shuganban Faransa Jacques Chirac ya yi alkawrin gyara kogin cikin shekaru uku, amma hakarsa ba ta cimma ruwa ba. 

Sai dai a yanzu, ana ganin babu makawa cewa, za a gyaran kogin na Seine saboda Faransa na son a gudanar da wasu wasanni na iyo a kogin  a yayin gasar ta Paris 2024 kuma tuni aka ware euro biliyan 1 da miliyan 400 saboda tsaftace kogin kadai. 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.