Isa ga babban shafi
Afghanistan

Dakarun Afghanistan sun kashe daya daga cikin shugabannin Al Qaeda

Dakarun Afghanistan sun sanar da kashe daya daga cikin manyan shugabannin kungiyar Al Qaeda da Amurka ke nema ruwa a jallo, Abu Muhsin al-Masari, yayin da gwamnatin kasar ke zargin kungiyar Taliban cewar har yanzu tana alaka da kungiyoyin ‘Yan ta’adda.

Jami'an sojin Afghanistan
Jami'an sojin Afghanistan REUTERS/Omar Sobhani
Talla

Hukumar leken asirin kasar ta bayyana al-Masari wanda dan kasar Masar ne a matsayin shugaba na biyu a Yankin India dake jagorancin kungiyar, kuma an hallaka shi ne a Yankin Ghazni.

Ministan cikin gida Masoud Andarabi yace kashe al-Masari ya dada fito da dangantaka tsakanin Taliban da Al Qaeda dake yakar gwamnatin Afghanistan.

Baiwa mayakan Al Qaeda wurin zama shine dalilin da ya sa Amurka ta kaddamar da hare hare da mamaye kasar Afghanistan bayan harin da aka kai mata na 11 ga watan Satumabr shekarar 2011.

Yanzu haka Amurkar da kungiyar Taliban sun kulla yarjejeniyar zaman lafiya wanda zai sa dakarun Amurka da NATO su fice daga cikin kasar.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.