Isa ga babban shafi
Mexico

Mexico: Girgizar kasa ta hallaka sama da mutane 200

Girgizar kasa mai karfin gaske da ta aukawa tsakiyar kasar Mexico, tayi sanadin mutuwar sama da mutane 200, tare da rusa daruruwan gidaje.

Wasu jami'an ceto a garin Mexico City da girgizar kasa ta aukawa.
Wasu jami'an ceto a garin Mexico City da girgizar kasa ta aukawa. REUTERS/Henry Romero
Talla

Shugaban kasar Enrique Peña Nieto, ya ce sama da kanan yara 20 suka rasa rayukansu, yayinda wasu 30 suka bace bayanda makarantarsu ta rubza.

Girgizar kasar mai karfin maki 7.1 da ta jijjiga makwabtan ihohin Mexico City, ta auku ne jim kadan bayan daruruwan ‘yan kasar ta Mexico, sun kammala karbar horon ceto da kuma bada agajin gaggawa a duk lokacin da aka samu girgizar kasa.

Ko a farkon watan Satumba, sai da wata girgizar kasar mai karfin maki 8.1 da ta aukawa kudancin kasar ta hallaka mutane 90.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.