Isa ga babban shafi
Amurka

Trump ya janye tallafin da Amurka ke baiwa wasu kasashe 3

Shugaban Amurka Donald Trump, ya janye tallafin da yake baiwa kasashen, El Salvador, Guatemala da Honduras, bayan da ya zargi kasashen da turawa Amurka ‘yan ci rani.

Shugaban Amurka Donald Trump.
Shugaban Amurka Donald Trump. REUTERS/Carlos Barria
Talla

Trump ya dauki matakin ne, sa’o’i kalilan, bayan da yayi barazanar rufe kan iyakar Amurka da Mexico duk dai kan batun kwarar bakin hauren cikin Amurkan, matakin da Trump yace zai tabbata muddin kasar ta Mexico ta gaza dakatar da kwarar ‘yan ci ranin ta kan iyakarsu dake yankin kudanci.

A shekarar bara wata tawaga da ta kunshi ‘yan ci rani akalla dubu 7 ta taso daga kasar Honduras da nufin zuwa Amurka, inda tuni suka isa kasar Mexico da ke makwabtaka da ita, abinda shugaba Trump ya bayyana shi a matsayin al’amarin da aka shirya shi da gangan.

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.