Trump ya janye tallafin da Amurka ke baiwa wasu kasashe 3
Shugaban Amurka Donald Trump, ya janye tallafin da yake baiwa kasashen, El Salvador, Guatemala da Honduras, bayan da ya zargi kasashen da turawa Amurka ‘yan ci rani.
Wallafawa ranar:
Trump ya dauki matakin ne, sa’o’i kalilan, bayan da yayi barazanar rufe kan iyakar Amurka da Mexico duk dai kan batun kwarar bakin hauren cikin Amurkan, matakin da Trump yace zai tabbata muddin kasar ta Mexico ta gaza dakatar da kwarar ‘yan ci ranin ta kan iyakarsu dake yankin kudanci.
A shekarar bara wata tawaga da ta kunshi ‘yan ci rani akalla dubu 7 ta taso daga kasar Honduras da nufin zuwa Amurka, inda tuni suka isa kasar Mexico da ke makwabtaka da ita, abinda shugaba Trump ya bayyana shi a matsayin al’amarin da aka shirya shi da gangan.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu