Adadin wadanda suka mutu saboda Ebola sun kai 55 a Congo
Ma’aikatar kiwon lafiya a Jamhuriyar Dimokuradiyyar Congo, ta ce adadin wadanda suka rasa rayukansu sakamakon kamuwa da cutar Ebola sun hai 55 a halin yanzu.
Wallafawa ranar:
Alkawalumman da ma’aikatar lafiyar ta fitar, ta ce mafi yawan wadanda suka rasa rayukansu na zaune ne a yankin Kivu ta Arewa, yankin da ke fama da rikici na tsawon shekaru, lamarin da ke kara haifar da tarnaki ga jami’an kiwon lafiya da ke kokarin isa ga wadanda suka kamu da cutar.
Yanzu haka dai hukumar lafiya ta duniya na ci gaba da kokari domin tabbatar da cewa cutar ba ta yaduwa zuwa sauran sassa na kasar ba.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu