Isa ga babban shafi
Najeriya-Afrika ta Kudu

Za a hukunta 'yan sandan da suka kashe dan Najeriya

Yau ake sa ran hukumomin Afrika ta Kudu za su gurfanar da jami’an ‘yan sandansu guda 8 da ake tuhuma da laifin kashe wani dan Najeriya, Ibrahim Badmus, bayan azabtar da shi a watan Oktoban bara.

Ana zargin jami'an 'yan sandan Afrika ta Kudu da yawan cin zarafin baki
Ana zargin jami'an 'yan sandan Afrika ta Kudu da yawan cin zarafin baki AFP PHOTO / ALEXANDER JOE
Talla

A karshen makon da ya gabata ne wata tawagar ‘yan sanda ta musamman ta cafke wadannan jami’an da ake zargi da kisan Badmus da suka hada da Ms. Catherine Tenteza, Ms. Gerhard Der-Walt, Mr. Nkosinathi Ngwenya, Mr. Aaron Arends, Mr. Nomkhosi Khoza, Mr. Emmanuel Ngwane, Mr. Msebenzi Mkhuma da kuma Mr. Joseph Mamasela

Jakadan Najeriya a kasar Godwin Adama ya ce matakin zai karfafa gwuiwa ga ‘yan kasashen waje da ke zama a Afrika ta Kudu da ke zargin jami’an tsaro da cin zarafinsu.

‘Yan Najeriya sun nuna bacin ransu matuka da kisan Badmus, yayin da a farko ‘yan sandan suka ce, wasu masu fataucin miyagun kwayoyi ne suka kashe shi.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.