Isa ga babban shafi
Algeria

Bouteflika zai yi murabus a cikin watan Afrilu

Fadar gwamnatin Algeria ta ce shugaban kasar AbdelAziz Bouteflika zai yi murabus kafin ranar 28 ga watan Afrilu, lokacin da wa’adinsa zai kare.

Shugaban kasar Algeria Abdelaziz Bouteflika.
Shugaban kasar Algeria Abdelaziz Bouteflika. Reuters
Talla

Matakin amincewa da yin murabus din Bouteflika, ya zo ne bayan da manyan jam’iyyun siyasar kasar cikin har da tasa, suka goyi bayan dubban ‘yan kasar da ke zanga-zangar neman tilasta masa sauka daga mulki.

Cikin sanarwar da ta fitar a yau Litinin, fadar Gwamnatin ta Algeria ta ce shugaba Bouteflika mai shekaru 82 zai sauka ne bayan daukar wasu muhimman matakai, wadanda ba a bayyana ba.

Matsin lambar tilastawa Bouteflika yin murabus ya soma ne bayanda shugaban ya bayyana aniyar neman wa’adi na 5 a babban zaben kasar da a baya aka tsara zai gudana a ranar 18 ga watan Afrilu.

Bayan zafafar zanga-zangar dubban ‘yan Algeria, Bouteflika ya janye aniyarsa ta neman tazarce, amma da sharadin dage zabukan kasar zuwa wani lokaci da bai bayyana ba.

Matakin shugaban na Algeria ya sake tunzara masu zanga-zangar wadda dubban dalibai da malamansu da kuma manyan lauyoyi suka shiga.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.