Isa ga babban shafi
Saudi-Yemen

'Yan tawayen Houthi sun yi barazanar kai hari muhimman gurare a Saudiya

Shugaban 'Yan Tawayen Houthi da ke Yemen, Abdulmalik al-Huthi ya yi gargadin cewar suna iya kai hari muhimman wuraran dake Saudi Arabia da Daular Larabawa dake jagorancin yaki akan su yanzu haka.

Mayakan 'yan tawayen Houthi na Yemen
Mayakan 'yan tawayen Houthi na Yemen REUTERS/Khaled Abdullah/File Photo
Talla

Al Huthi ya ce 'yan Tawayen a shirye su ke su ci gaba da kai hare hare kan dakarun kawancen da ke kai musu hari a yakin da aka kwashe shekaru 4 ana fafatawa, kuma makaman su masu linzami na iya kai wa Riyadh da Abu Dhabi da kuma Dubai.

Yayin wata hira da aka yada ta kafar talabijin, shugaban 'Yan Tawayen ya ce a shirye dakarunsu su ke a kasa da kuma bakin daga, kuma a shirye suke su sadaukar da rayukan su.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.