Isa ga babban shafi
Gambia

Gambia ta fice daga Kungiyar renon Ingila

Kasar Gambia ta sanar da ficewar ta daga kungiyar kasashe renon Ingila, bayan ta kwashe shekaru 48 a matsayin Mamba. Shugaba Yahya Jammeh, ya bayyana kungiyar a matsayin wani dubaru na mulkin mallaka don ci gaba da jan ragamar yadda ake gudanar da mulki a kasashen Afrika.

Yahya Jammeh shugaban kasar Gambia
Yahya Jammeh shugaban kasar Gambia IISD/Earth Negotiations Bulletin/Wikimedia Commons
Talla

Shugaban ya dade yana zargin Birtaniya da tallafawa ‘Yan adawar kasarsa, wanda ake zargi yana keta hakkin bil’adama.

Kungiyar Commonwealth ta kunshi kasashe sama da 50 wadanda gwamnatin Birtaniya ta yi wa mulkin Mallaka. Sai dai kuma babu wani cikakken bayani da gwamnatin Gambia ta bayar game da matakin ficewa daga kungiyar.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.