Sojojin Masar sun bukaci Sisi ya tsaya takara
Babbar Majalisar Koli ta Sojin kasar Masar ta bayyana goyon bayanta ga Janar Abdel-fattah al-Sisi, ya tsaya takarar shugaban kasa wanda ake ganin babu tantama zai lashe, wanda ya hambarar da gwamnatin dimokuradiya ta Mohammed Morsi na Jam’iyyar ‘yan Uwa Musulmi a watan Yulin bara.
Wallafawa ranar: Chanzawa ranar:
Al-Sisi yanzu ana jiran ya tube kakin Soji ne domin ya tsaya takarar zaben shugaban kasa da za’a gudanar a watan Afrilu.
Wannan na zuwa ne bayan mutane da dama sun mutu a wata arangama da aka yi tsakanin Jami’an tsaro da magoya bayan ‘Yan musulmi a karshen mako.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu