Isa ga babban shafi
Guinea

Cutar Ebola ta kashe mutane 208 a Guinea-WHO

Hukumar lafiya ta Duniya WHO, tace adadin mutanen da suka mutu sanadiyar cutar Ebola a kasar Guinea, sun kai 2008, tare da kwatanta cutar a matsayin mafi muni da ta auku tun bulluwarta.

Likitoci da ke kula da cutar Ebola a Guinea
Likitoci da ke kula da cutar Ebola a Guinea AFP PHOTO / MEDECINS SANS FRONTIERES
Talla

Hukumar tace akwai mutane 328 da aka tabbatar da suna dauke da cutar a Guinea cikinsu har da 208 da suka mutu. Cutar kuma yanzu ta yadu zuwa kasar Saliyo da Liberia.

Hukumar WHO tace mutane 79 ne suka kamu da cutar a kasar Saliyo. A kasar Liberia kuma mutane 6 ne aka ruwaito sun mutu.

Likitoci sun ce cutar na yaduwa ne saboda mutane ba su son zuwa Asibiti, suna dogaro da maganin gargajiya.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.