Isa ga babban shafi
Amurka-saliyo

Amurka na daukan matakan warware rikicin siyasar saliyo

Ma’aikatar Harkokin wajen Amurka tace tana daukar matakan da suka dace dan warware rikicin siyasar kasar Saliyo bayan da mataimakin shugaban kasar ya nemi mafakar siyasa a ofishin Jakadancin ta

Tutar Amurka
Tutar Amurka
Talla

Mai Magana da yawun ma’aikatar Darby Holladay, tace ya zuwa yanzu dai mataimakin shugaban kasar Saliyo Samuel Samsumana baya ofishin Jakadancin ta dake Freetown, inda tayi kira ga bangarorin siyasar kasar da suyi anfani da kundin tsarin mulkin kasar dan warware takaddamar.

Mataimakin shugaban kasar yace sojoji sun mamaye gidan sa a karshen mako bayan Jam’iyyar su ta APC ta kore shi saboda zargin tada hankali.

Ya zuwa yanzu dai ba’a san inda ya buya ba.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.