Togo
Mutane biyu sun mutu a tarzomar kasar Togo
Hankula sun kwanta a garin Mongo da ke arewacin kasar Togo, inda a jiya juma’a aka gudanar da tarzoma wadda ta yi sanadiyyar samun asarar rayukan akalla mutane biyu.
Wallafawa ranar:
Talla
Tarzomar dai ta barke ne bayan da hukumomin kasar suka bayar da izinin ware wani katafaren fili domin makiyaya a gabar ruwan wani kogi da ke yankin.
Manona da masunta da ke kiran kansu ‘yan asalin yankin sun nuna rashin amincersu da haka, inda daga bisani aka yi amfani da jami’an tsaro domin kwantar da hankula.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu