Burundi
Tattaunawar zaman lafiyar Burundi ta watse
Shirin tattaunawar zaman lafiya tsakanin gwamnatin Burundi da 'yan adawar kasar a Tanzania ya watse sakamakon janyewar wakilan gwamnatin kasar.
Wallafawa ranar:
Talla
Taron wanda tsohon shugaban kasar Tanzania Benjamin Mkapa ke jagoranta don kawo karshen tashin hankalin da ya lakume rayuwar mutane kusan 500, na gamuwa da cikas ne saboda yadda bangaren gwamnati ke jan kafa akai.
Akalla mutane 270,000 suka gudu suka bar Burundi don kaucewa tahsin hankalin da ake fama da shi a kasar.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu