Isa ga babban shafi
Libya

An gano gawarwakin mutane 74 a gabar teku

Kungiyar Agaji ta Red Crescent tace an gano gawarwakin wasu baki 74 da suka mutu a tekun meditareniyan yayin da suke kokarin tsallakawa zuwa nahiyar Turai daga Libya.

Jami'an kungiyar agaji ta Red Crescent a Libya da ke kwashe gawarwakin da aka gano a gabar teku.
Jami'an kungiyar agaji ta Red Crescent a Libya da ke kwashe gawarwakin da aka gano a gabar teku. Libyan Red Crescent /nytimes
Talla

Kungiyar tace mazauna kauyen Harcha dake wajen garin Zawiya mai nisan kilomita 45 daga Tripoli suka shaidawa masu aikin agaji gano gawarwakin, bayan ruwan ya turo su gabar teku.

Kungiyar dake sa ido kan baki tace ranar lahadi wani kwale kwalen mai dauke da mutane kusan 100 ya kife a takun na Meditareniyan.

Kakakin hukumar lura da ‘yan gudun hijira ta duniya IOM, Flavio Di Giacomo ya ce, binciken da suka gudanar ya nuna cewa, an bar kwale kwalen robar dauke da bakin, yana watangaririya a kan teku tsawon kwanaki bayan lalacewar injinsa.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.