Dan Masanin Kano Maitama Sule ya rasu
Allah Ya yi wa Dakta Yusuf Maitama Sule Dan Masanin Kano rasuwa a yau Litinin bayan ya dade yana fama da rashin lafiya. Rahotanni sun ce ya rasu ne a kasar Masar bayan an tafi da shi domin diba lafiyarsa.
Wallafawa ranar: Chanzawa ranar:
Alhaji Maitama Sule ya rasu yana da shekaru 87 a duniya.
A cikin wata sanarwa da gwamnatin Kano ta fitar, ta ce da misalin karfe 4 na yamma bayan Sallar La'asar za a yi Jana'izarsa a fadar Sarkin Kano.
Sannan Gwamnatin Kano ta ware gobe Talata a matsayin ranar hutu domin jimamin rasuwar Dan Masani.
Dan Masanin Kano fitacce ne a Najeriya a siyasance da kuma diflomasiya. Ya taba tsayawa takarar shugaban kasa a Jam’iyyar Alhaji Shehu Shagari ta NPN.
Sannan ya taba rike mukamin Minista da jekadan Najeriya a Majalisar Dinkin Duniya.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu