Isa ga babban shafi
Kenya

'Yan Sandan Kenya sun tarwatsa 'yan adawa a Nairobi

Jami’an ‘yan sandan Kenya sun yi amfani da hayaki mai sa-kwalla wajen tarwatsa dandazon ‘yan adawa da ke zanga-zanga a birnin Nairobi a wannan Litinin.

'Yan sandan Kenya sun tarwatsa 'yan adawaa da ke zanga-zanga a birnin Nairobi
'Yan sandan Kenya sun tarwatsa 'yan adawaa da ke zanga-zanga a birnin Nairobi REUTERS/Goran Tomasevic
Talla

‘Yan adawar dai na bukatar gwamnati da ta kori jami’an hukumar zaben kasar da aka zarga da tafka magudi a zaben shugabancin kasar da aka gudanar.

Kazalika rahotanni sun ce, ‘yan sandan sun dauki irin wannan mataki na harba barkonon tsohuwa a yammacin birnin Kisumu.

Ana saran sake gudanar da zaben shugabancin Kenya a ranar 26 ga wannan wata na Oktoba bayan Kotun Koli ta soke zaben farko da aka gudanar a cikin watan Agusta saboda kura-kuren da ta ce an samu.

Za a dai sake fafatawa tsakanin shugaba mai ci Uhuru Kenyatta da abokin hamayyarsa Raila Odinga.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.