Raila Odinga ya janye daga zaben Kenya
Jagoran ‘yan adawa a Kenya Raila Odinga, ya sanar da janyewa daga zaben shugabancin kasar da aka tsara gudanarwa a ranar 26 ga wannan wata na oktoba.
Wallafawa ranar:
A sanarwar da ya yi dazun nan a birnin Nairobi, Odinga ya ce ya dauki matakin janyewar ne saboda kare muradun kasar ta Kenya da kuma na al’ummarta.
Odinga da ya nuna shakku kan yi masa adalci a zaben da za a yi a nan gaba, ya bayyana rashin gamsuwarsa da irin matakan da hukumar zabe ta kasar ke dauka.
Raila Odinga yayin sanar da janyewa daga zaben kenya da za a maimaita
Press Conference https://t.co/JCc7Uij37L
Raila Odinga (@RailaOdinga) October 10, 2017
A watan da ya gabata kotun kolin kasar ta soke zaben shugabanci kasa da aka gudanar a ranar 8 ga watan Agusta kuma ya bai wa shugaba mai ci Uhuru Kenyatta Nasara kan wasu kura-kurai da ta ce an tafka.
Shugaba Kenyatta ya ce bai karaya ba da wannan hukunci da Odinga ya dauka na janye takararsa.
Martanin Shugaba Uhuru Kenyatta kan janyewar Odinga daga zabe
What is the justice in the act of withdrawing from an election after causing Kenyans to use Kenya shillings 12 billion? #VoiNiJubilee pic.twitter.com/4DqWR6T3BN
Uhuru Kenyatta (@UKenyatta) October 10, 2017
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu