Isa ga babban shafi
kenya

An kashe masu zanga-zanga a Kenya

‘Yansanda a kasar Kenya sun tabbatar da mutuwar mutane biyu bayan da kotun kolin kasar ta yanke hukuncin amincewa da zaaben da aka yi wa Uhuru Kenyatta a matsayin shugaban kasa.

Rikicin zaben shugaban kasar Kenya a janyo rasa rayuka.
Rikicin zaben shugaban kasar Kenya a janyo rasa rayuka. REUTERS/Baz Ratner
Talla

A ranar Litini ne kotun ta sanar da matsayarta bayan sauraron korafe-korafen da aka shigar a gabanta daga bangaren ‘yanadawa.

'Yandsanda sun rinka harbi domin tarwatsa magoya bayan ‘yan'adawar kasar masu zanga-zanga a yankin Kisumu.

Mutum daya ne aka tabbatar ya halaka a unguwar marasa galihu ta Kibera da ke birnin Nairobi, yayin da aka harbe wani a yammacin yankin Migori.

A bangare daya kuma, kade-kade da raye-raye ne suka barke, musamman ma a tsakanin magoya bayan shugaba Uhuru Kenyatta, wanda kotu ta bai wa nasara.

A ranar Litini ne kotu ta bayyana cewa korafe-korafen da aka shigar gabanta na neman soke zaben ba su da kwari.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.