An soma shari’ar wasu mayakan Boko Haram a Nijar
Wata Kotun kasa da kasa ta musamman dake birnin Yamai a Jamhuriyar Nijar, ta soma shari’ar wasu mutane takwas da ake zargi da zama mayakan kungiyar Boko Haram.
Wallafawa ranar:
Karo na farko kenan kotun ta fara shari’ar a fili, sabanin yadda ta ke gudanar da shari’a a baya cikin sirri, matakin da kungiyoyin kare hakkin dan adam suka dade suna suka.
Mutanen da suka gurfana a gaban kotun sun fito ne daga Nijar, Najeriya da kuma Chadi, wadanda ake zargin su da bai wa kungiyar Boko Haram gagarumar gudunmawa.
Kararraki 22 kotun musamman din da ke Yamai zata saurara, nan da kwanaki 10 masu zuwa, bayan shari’ar da ta yiwa akalla mutane 300 da ake zargin mayakan Boko Haram ne a shekarar 2017 da ta gabata.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu