Isa ga babban shafi
Nijar

An soma shari’ar wasu mayakan Boko Haram a Nijar

Wata Kotun kasa da kasa ta musamman dake birnin Yamai a Jamhuriyar Nijar, ta soma shari’ar wasu mutane takwas da ake zargi da zama mayakan kungiyar Boko Haram.

Wasu daga cikin mayakan Boko Haram
Wasu daga cikin mayakan Boko Haram REUTERS/Zanah Mustapha
Talla

Karo na farko kenan kotun ta fara shari’ar a fili, sabanin yadda ta ke gudanar da shari’a a baya cikin sirri, matakin da kungiyoyin kare hakkin dan adam suka dade suna suka.

Mutanen da suka gurfana a gaban kotun sun fito ne daga Nijar, Najeriya da kuma Chadi, wadanda ake zargin su da bai wa kungiyar Boko Haram gagarumar gudunmawa.

Kararraki 22 kotun musamman din da ke Yamai zata saurara, nan da kwanaki 10 masu zuwa, bayan shari’ar da ta yiwa akalla mutane 300 da ake zargin mayakan Boko Haram ne a shekarar 2017 da ta gabata.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.