Zimbabwe
Za'a Binne Gawan Madugun Adawa Morgan Tsvangirai Ranar Talata
An kammala dukkan shiri domin binne gawan madugun adawa na kasar Zimbabwe Morgan Tsvangirai a kauyensa Buhera ranar Talata. Asabar aka kai gawansa Zimbabwe daga kasar Africa ta Kudu inda ake duba lafiyarsa.
Wallafawa ranar:
Talla
Morgan Tsvangirai ya mutu yana da shekaru 65 bayan yayi fama da cutar daji.
Daruruwan jama'a suka tarbi gawansa a lokacin da aka kai ta Harare daga kasar Africa ta kudu.
Ana yiwa Morgan Tsvangirai kallon dan adawa mara tsoro da yake sukan jamiyar dake mulkin Zimbabwe ZANU-PF.
Za'a binne shi a kauyensa Buhera mai kimanin nisan kilomita 250 daga Harare.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu