Jean-Pierre Bemba zai koma gida gabannin babban zabe
Jam’iyyar tsohon mataimakin shugaban kasar Jamhuriyar Dimokiradiyar Congo, Jean-Pierre Bemba, tace jagoran nasu zai koma gida ranar 1 ga watan Agusta domin tsayawa takarar zaben da za’ayi a karshen wannan shekara.
Wallafawa ranar:
Wata sanarwar da Jam’iyyar at rabawa manema labarai na dauke da cewar, bayan shekaru 10, shugaban su Sanata Jean-Pierre Bemba Gomba zai koma Congo, kasar kakannin sa ranar 1 ga watan Agusta.
Jam’iyyar ta bukaci magoya bayan su da su fitar farin dango domin tarbar shugaban wanda kotun hukunta manyan laifufuka ta wanke.
A farkon watan Yuli na wannan shekara ce jam’iyyar adawa da MLC, ta zabi kasar Jean Pierre Bemba, a matsayin dan takarar ta, a zaben shugabancin kasar, makwanni kadan bayan da kotun hukunta manyan laifuka ta duniya ICC, ta wanke shi daga zargin aikata laifukan yaki a Jamhuriyar Afrika ta tsakiya.
Takarar dai ka ‘iya zama babban kalubale ga gwamnatin shugaba Joseph Kabila, wanda ‘yan adawa ke zargin yana da aniyar sake tsayawa takara a zaben kasar na watan Disamba mai zuwa, bayan kin sauka daga mukaminsa da ya yi, duk kuwa da cewa wa’adinsa ya kare tun a shekarar da ta gabata.
Kin saukar Kabila da ke shugabantar Jamhuriyar Congo tun daga shekarar 2001 ya haddasa jerin zanga-zanga a kasar, da sukai sanadin hallakar rayukan 'yan kasar da dama da ke neman tilastawa shugaban yin murabus.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu