Isa ga babban shafi
Burkina-Faso

Rikici ya hallaka mutane 46 a Burkina Faso

Rahotanni daga Burkina Faso na cewa akalla mutane 46 ne suka mutu cikin makon nan sakamakon hare-haren mayaka masu ikirarin jihadi da kuma rikicin kabilanci a sassan tsakiyar kasar.

Shugaban kasar Burkina Faso Roch Marc Christian Kaboré.
Shugaban kasar Burkina Faso Roch Marc Christian Kaboré. ©SIA KAMBOU/AFP
Talla

Tun farko dai mahukuntan kasar sun sanar da mutuwar mutane 13 sakamakon rikicin da ya barke a kauyen Yirgou na yankin Barsalogo a ranakun Talata da Laraba, sai dai kakakin gwamnatin kasar ya ce adadin wadanda suka mutun ya karu zuwa 46 a yau Juma’a.

A cewar kakakin gwamnatin Remis Fulgance rikicin ya faro ne daga wani harin ‘yan bindiga da ya hallaka mutane 7 cikin har da shugaban kauyen.

Sai dai kuma barkewar sabon rikici bayan harin a cewarsa ya haddasa asarar tarin rayuka wanda a yau ya kai 46.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.