Jam'iyyar ANC ta shirya tsaf domin tunkarar zaben yan Majalisu
A Afrika ta kudu jam’iyyar ANC da ta jima ana damawa da ita a fagen siyasar kasar a jiya asabar ta gabatar da da sabon tsari da ta shirya domin tunkarar zabukan yan majalisun kasar na watan Mayu.
Wallafawa ranar:
Shugaban kasar Cyril Ramaphosa da kan sa ne ya kaddamar da sabuwar tafiya domin tunkarar zabukan yan majalisu na watan Mayu na wannan shekara .
Shugaban ya bayyana fatan sa na samun goyan baya daga yan kasar don samun rijayen da ya dace a zauren Majalisa.
Jam’iyyar a yan shekaru da suka gabata ta fuskanci matsalloli da suka jibanci cin hanci da rashawa,wanda ya janyo korar wasu daga cikin ya’an jam’iyyar.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu