An Kawo karshen tuhumar da ake yiwa wasu yan Equatorial Guinea
Hukumomin Malabo na kasar Equitorial Guinea sun jingine ci gaba da tuhuman da ake yiwa wasu mutane fiye da 150 da ake zargin suna da hannu wajen kulle-kullen juyin mulki da bai yi nasara ba, a watan 12 na shekara ta 2017.
Wallafawa ranar:
Ponciano Mbomio Nvo daya daga cikin lauyoyi 16 dake kare mutanen ya fadi cewa Hukumomin kasar basu ce upon ba dangane da ci gaba ko kuma dakatar da wannan tuhuma.
Tun watan Maris na bara mutanen ke tsare bisa zargin kulla kiffar da Gwamnatin shugaba Teodoro Obiang Nguema wanda hukuncin kisa ne kawai.
Shugaba Theodoro na daga cikin Shugabanin da suka fi jimawa a karagar mulkin kasa a Afrika,wanda ake kuma ake dangantawa da mai mulkin kama kariya,kasancewa yan adawa ba su da nafa a ji a fagen siyasa.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu