Jami'an tsaron Sudan sun kame shugabannin 'yan adawa
Jami’an tsaron Sudan sun kame wasu tsaffin ’yan tawayen kasar 2, da kuma jagoran yan adawa 1, kwanaki kalilan bayan tarwatsa masu zanga-zanga da ke neman sojoji su mika mulki ga farar hula.
Wallafawa ranar:
A ranar Litinin 3 ga watan Yuni, jami'an tsaron Sudan suka hallaka sama da mutane 100, yayin murkushe masu zanga-zanga da ke zaman dirshan a birnin Khartoum.
Kame tsaffin jagororin yan tawayen da jagoran na yan adawa ya zo ne, sa’o’i kadan, bayan da suka gana da Fira Ministan Habasha Abiy Ahmed a Khartoum, wanda a jiya Juma’a ya isa birnin domin sansanta shugabannin masu zanga-zangar da bangaren sojoji wajen maido da tattaunawar da suka yi watsi da ita.
Rahotanni sun ce jami’an tsaron kwantar da tarzoma na Sudan da a baya aka fi sani da mayakan Janjawid ne suka kai samamen da aka damke shugabannin.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu