Isa ga babban shafi
Chadi-AU

Kungiyar AU ta bukaci shugabancin mulkin Soji a Chadi ya cika alkawari

Kungiyar kasashen Afirka ta AU ta bukaci shugabannin mulkin sojin Chadi da su tabbatar da mika mulki ga fararen hula a cikin watanni 18 masu zuwa bayan sun karbi ragamar tafiyar da kasar sakamakon rasuwar shugaba Idris Deby.

Shugaban gwamnatin Soji a Chadi Mahamat Idriss Déby Itno.
Shugaban gwamnatin Soji a Chadi Mahamat Idriss Déby Itno. © REUTERS - STRINGER
Talla

Sanarwar kungiyar ya bayyana rashin amincewar sa da duk wani yunkuri na kara wa’adin gwamnatin Sojin bayan kammala watanni 18.

Majalisar mulkin sojin da ke karkashin Janar Mahamat Deby, wanda ‚da ne ga marigayi shugaban kasar, ta kafa majalisar mulkin da ta kunshi sojoji da fararen hula, yayin da ta sanar da murkushe 'yan tawayen da ake zargi da kashe tsohon shugaban kasar.

Deby da ya jagorancin Chadi na shekaru 30 ya rasu ne sakamakon harin da 'yan tawayen FART suka kaddamar akan dakarun gwamnati.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.