Isa ga babban shafi

An kori alkalin kotun kolin Equatorial Guinea saboda rashawa

Shugaban Equatorial Guinea Teodoro Obiang Nguema Mbasogo, ya ce ya sallami alkalin kotun kolin  kasar biyo bayan amsa laifin karbar na goro a badakalar sauya lokacin lalacewar  kayayyakin abinci da magunguna da ya yi.

Teodoro Obiang, shugaban Equatorial Guinea.
Teodoro Obiang, shugaban Equatorial Guinea. Lusa
Talla

Shugaba Mbasogo, wanda ya shafe kusan shekaru 43 yana mulkin kasar ya sallami  alklin kotun kolin, David Nguema Obiang Eyang ne sakamakon kama shi da laifin saba ka’idojin aikinsa.

Mataimakin shugaban kasar, Teodoro Nguema Obiang Mangue, wanda da ne ga shugaba Mbasogo ya wallafa a shafinsa na Twitter cewa Eyang ya amsa laifin karbar Cfa miliyan 100 a matsayin toshiyar baki daga wani babban kamfani a kasar.

Babu alamun da ke nuna cewa alkalin zai gurfana a gaban kuliya sakamakon wannan laifi da ya amsa.

An ci tarar kamfanin da ya bada wannan toshiya Cfa miliyan 411, kana aka lalata kayayyakin da aka sauya lokacin lalacewarsu.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.