Isa ga babban shafi

Malawi na fama da karancin alluran rigakafin kwalara bayan tsanantar cutar

Dai dai lokacin da Malawi ke fama da mafi munin annobar kwalara wadda ke ci gaba da kisa a sassan kasar, ma’aikatar lafiya ta sanar da karancin allurar rigakafin wannan cuta da ke sanya amai da gudawa.

Cutar ta kashe mutane fiye da 600 daga bullarta zuwa yanzu.
Cutar ta kashe mutane fiye da 600 daga bullarta zuwa yanzu. AFP - MAURICIO FERRETTI
Talla

Kakakin ma’aikatar lafiyar kasar Adrian Chikumbe ya bayyana cewa kasar ba ta da wadatttun alluran rigakafin cutar ta kwalara a kasa da za ta yi amfani da su wajen dakile yaduwar cutar.

A watan Nuwamba ne Malawi ta karbi allurai miliyan 2 da dubu 900 daga kamfanin harhada magunguna na Gavi sai dai tsanantar cutar wadda ta fara bulla tun a watan Maris din bara cikin sassan kasar 29 ya haddasa karancin alluran.

Bisa alkaluman ma’aikatar lafiya a jiya juma’a dai kasar na da mutane 631 da suka mutu sanadiyyar cutar ta kwalara daga bullarta zuwa yanzu ciki har da wasu 17 da ta kashe a jiyan, yayinda a jummalla kasar ke da mutum dubu 28 da 132 da 916 wadanda ke jinyar cutar yanzu haka.

Ko a watan jiya sai da hukumar lafiya ta Duniya WHO ta yi gargadi kan yadda cutar ke tsananta a kasar, wadda ta ce wajibi ne a dauki matakan gaggawa don dakile yaduwarta zuwa sauran sassan kasar.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.