Isa ga babban shafi

Kotun ta samu kararraki shida da ke kalubalantar sakamakon zaben Oyo

Kotun sauraren kararrakin zabe a jihar Oyo da ke Najeriya ta karbi kararraki biyu dangane da zaben gwamna da hudu na zaben ‘yan majalisar dokoki.Sakataren kotun, Ibrahim Sada ne ya bayyana hakan a wata hira da kamfanin dillancin labarai na Najeriya NAN a ranar litinin a Ibadan.

Hukumar zaben Najeriyar mai zaman kanta INEC a matakin jihohi ta fara sanar da wadanda suka yi nasara a zaben gwamnonin kasar da ya gudana
Hukumar zaben Najeriyar mai zaman kanta INEC a matakin jihohi ta fara sanar da wadanda suka yi nasara a zaben gwamnonin kasar da ya gudana REUTERS/Adelaja Temilade
Talla

Ibrahim Sada ya ce karar farko na adawa da sakamakon zaben gwamna, jam’iyyar Allied People’s Movement (APM) da dan takararta, Adeniran Oluwaseyi ne suka shigar da karar, yayin da Action Alliance (AA) da dan takararta, Babatunde Ajala suka shigar da kara ta biyu.

Sakataren ya ce an shigar da karar ne a kan sanarwar da hukumar zabe mai zaman kanta ta Kasa (INEC) ta yi na bayyana Gwamna Seyi Makinde a matsayin wanda ya lashe zaben gwamnan da aka yi a ranar 18 ga Maris.

Jami'an hukumar zaben Najeriya INEC, yayin kirga kuri'un da aka kada a jihar Lagos.
Jami'an hukumar zaben Najeriya INEC, yayin kirga kuri'un da aka kada a jihar Lagos. AP - Sunday Alamba

Ya ci gaba da cewa, jam’iyyar PDP da dan takararta na mazabar jihar Orelope, Olowokere Adewale ne suka shigar da karar majalisar dokokin jihar.

Ibrahim Sada ya ce sauran wadanda suka shigar da kara sun hada da jam’iyyar All Progressives Congress (APC) da dan takararta na mazabar Ogbomoso ta Kudu, Adegoke Ayodeji; New Nigeria People’s Party (NNPP) da dan takararta na mazabar Ogbomoso ta Kudu, Adeniyi Oluwaseun.

Shugaban hukumar INEC farfesa Mahmud Yakubu kenan, lokacin da yake karbar sakamakon jihohi na zaben shugabancin kasar da aka yi ranar 25 ga watan Fabrairu, 2023.
Shugaban hukumar INEC farfesa Mahmud Yakubu kenan, lokacin da yake karbar sakamakon jihohi na zaben shugabancin kasar da aka yi ranar 25 ga watan Fabrairu, 2023. AP - Ben Curtis

Har ila yau, an samu wata takardar koke daga jam’iyyar PDP da dan takararta na mazabar Saki ta Yamma, Okedoyin Julius, na kalubalantar sakamakon zaben majalisar dokokin jihar, in ji sakataren.

Ya ce wa’adin kwanaki 21 da doka ta kayyade na shigar da kararrakin wadanda ba su ji ba basu gani ba ya ci tura, ya kara da cewa ba za a sake shigar da wata sabuwar kara ba.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.