Isa ga babban shafi

Yau za a fara gasar kwallon kafa ta nahiyar Afrika a Ivory Coast

A wannan asabar ake fara gasar kwallon kafa ta cin kofin nahiyar Afrika a Ivory Coast, inda mai masaukin bakin za ta barje gumi a wasan farko da Guinea Bissau.

Kwallon kafa
Kwallon kafa © pepifoto / IStock
Talla

Ivory Coast, wadda ta taba lashe wannan kofin a shekarar 1993 da 2015, za ta fafata da takwararta Guinea Bissau ne a filin wasa na Alassane Ouattara mai daukar 'yan kallo dubu 60.

Za a karkare gasar ta AFCON karo na 34 da wasan karshe da za a yi a ranar 11 ga watan Fabrairu.

A ranar 27 ga watan Janairu ne za a fara wasannin matakin sili daya kwale, a kuma buga wasannin daf-da-na-kusa-da -karshe a ranar 2 ga watan Fabrairu, sai kuma wasannin kusa da karshe da za a fafata a ranar 7 ga watan Fabrairu.

Kasar Masar, wadda za a dama da ita a wannan gasa, ita ce ta fi kowace kasa cin wannan gasa, inda sau 7 tana lashe kofin, Sai kamaru mai bi mata da kofuna 5, sannan Ghana da kofuna 4 sai kuma Najeriya da ta lashe kofuna 3.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.