Isa ga babban shafi
Iraqi

Blair ya sake neman afuwa akan mamayar Iraqi

Tsohon Firaministan Birtaniya Tony Blair ya nemi gafara kan mamayar da suka yi wa kasar Iraqi da kuma kashe shugabanta Saddam Hussein a shekarar 2003, tare da danganta mamayar da haifar da mayakan IS da suka kwace ikon wasu yankunan Iraqi da Syria.

Tsohon Firaministan Birtaniya Tony Blair
Tsohon Firaministan Birtaniya Tony Blair REUTERS/Brendan McDermid
Talla

Sai dai Blair ya ce bai yi nadamar kawar da Saddam Hussian ba, amma ya nemi afuwa akan kuskurensu daga bayanan sirin da suka samu.

Blair ya amince da cewar mamayar da suka kai kasar ce ta haifar da mayakan ISIS a yau, wadanda suka zama barazana ga duniya baki daya.

A bayanan tosohon Firimiyan na Britaniya da aka wallafa a shafin kafar yada labarai ta CNN ya ce akwai kamshin gaskiya akan alakar mamayar da Amurka da Birtaniya suka yi wa Iraqi da kuma samuwar mayakan IS.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.