Isa ga babban shafi
Brazil

Brazil : An amince a tsige Rousseff a Majalisar Dattijai

Kwamitin da Majalisar Dattijan Brazail ta kafa domin nazari akan makomar shugabancin Dilma Rousseff ya amince a tsige shugabar da aka dakatar. ‘Yan majalisa 14 suka amince a kwamitin mai mambobi 19.

Dilma Rousseff ta Brazil
Dilma Rousseff ta Brazil AFP
Talla

Wannan matakin dai babbar baraka ce ga Rousseff, wanda zai kawo karshen faduwar gwamnatinta.

Ana zargin shugabar ne da kashe kudade ba bisa ka’idar doka ba tare karbar bashin bankuna a lokacin yakin neman zabe domin fadada ayyukan gwamnati a kasafin kudi.

Tuni dai aka nada babban mai adawa da ita Michel Temer a matsayin shugaban riko, kuma idan har aka tsige ta zai kasance shugaban Brazil har lokacin da za a yi zabe a 2018.

Wannan na zuwa ne a yayin da Brazil ke shirin bude wasannin Olympics a Rio.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.