Isa ga babban shafi
Columbia

Za a yi bikin cimma yarjejeniyar zaman lafiya a Colombia

A ranar 26 ga watan Satumba ne, gwamnatin Colombia za ta cimma yarjejeniyar zaman lafiya da kungiyar ‘yan tawayen FARC a hukumnce, kamar yadda shugaban kasar, Juan Manuel Santos ya sanar.

Shugaban kasar  Colombia, Juan Manuel Santos
Shugaban kasar Colombia, Juan Manuel Santos Foto: Reuters.
Talla

Mr. Santos ya ce, sanarwar cimma yarjejeniyar da nufin kawo karshen rikicin shekeru 50, ita ce mafi muhimmanci a rayuwarsa.

Shi ma shugaban ‘yan tawayen, Timoleon Timochenko ya sanar da ranar cimma yarjejeniyar a shafinsa na Twitter.

A na saran shugabannin kasashen yankin Latin Amurka za su halarci bikin cimma yarjejeniyar wanda za a yi a birnin Cartagena.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.