Isa ga babban shafi
Philippines

Aman-wutan dutse ya tilastawa Dubban mutane barin gidajensu a Philippines

Akalla Mutum dubu 90 ne suka tserewa rayukansu sakamakon aman-wutan dutse da ke barazanar a wasu yankunan Philippines, lamarin da mahukunta kasar ke cewar ya tsananta rashin tsafta a wuraren da mutanen ke samun mafaka.

Wani soja na tallafawa masu tsere wa gidajensu sakamakon aman wutan dutse da ke barazanar a wasu yankunan Philippines
Wani soja na tallafawa masu tsere wa gidajensu sakamakon aman wutan dutse da ke barazanar a wasu yankunan Philippines REUTERS/Stringer
Talla

Makonnin biyu kenan da kasar ta fara fuskantar iftila’I aman wutan dutsen, lamarin da ya tursasawa mahukunta kasar umartan mazauna kusa da tsaunin Mayon su nesanta kansu da akalla kilomita 5.6 daga tsaunin.

Wannan dalili ya sanya mutane da dama tururuwa zuwa yankunan tsira, lamarin da ya tsananta rashin tsafta saboda yawan mutane da suka taru a wuri guda.

A cewar Gwamnan lardin Albay, Al Franncis Bichara, mutane da aka bai wa mafaka a sansanonin za su bukaci akalla wata guda kafin su koma yankunansu.

Sai dai ya yi gargadi karancin kayayyakin tallafi, da kuma rashin mekewaye a matsugunan, inda ya ce mutum 200 na amfani da wuri guda wajen bahaya, alhalin ana bukatar bundakunan 1,222 domin amfani kowani mutum 50 a sansanin.

Shugaban Kasar Rodrigo Duterte da ya kai ziyarci yankin domin ganin halin da mutane ke ciki, ya nuna damuwarsa kan rashin mekewayen.

Wannan shine karo na 52 a cikin karni 4 da tsaunin Mayon da ke da tsayin Kilomita 330 a kudu maso gabashin Manila ke aman wuta. A shekara ta 1814 irin wannan iftila'in ya kashe mutum 1,200 lokacin da ya lulube garin Cagsawa.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.