Isa ga babban shafi
Syria-Amurka

Amurka za ta hukunta wanda ake zargi da kai harin guba a Syria

Shugaba Donald Trump na Amurka  yayi gargadin daukan tsatstsaurar mataki   muddin aka gano cewa da gaske ne an yi amfani da makamai masu guba a wani hari da aka kai garin Douma na kasar Syria.

Shugaba Donald Trump na Amurka a hagu sai kuma shugaban Syria Bashar Assad a dama.
Shugaba Donald Trump na Amurka a hagu sai kuma shugaban Syria Bashar Assad a dama. RFI
Talla

Kasashen duniya da dama dai sun nuna rashin jin dadin rahotanni dake nuna anyi amfani da makamai masu guba jim kadan bayan da ‘yan tawaye suka amince su bar garin Douma, wanda shi ne gari dake hannunsu na karshe.

Barazanar shugaba Trump na zuwa ne shekara daya chur da Amurka da chilla wani makami mai linzami sararin samaniyar Syria don maida martani game da harin makami mai guba na Sarin da aka kai kan fararen hula.

A sakon Trump na baya-bayan nan na cewa akwai mamata da yawa da suka hada da mata da yara kanana sakamakon hari da makamai masu guba a Syria.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.