Isa ga babban shafi
Philippines

Iska da Goguwa ta kashe mutane biyu a Philippines

Wata mahaukaciyar guguwa dauke  da ruwan sama mai karfin gaske da ake kira Super Typhoon Mangkhut ta dira a kasar Philippines, a yau Asabar inda ta fara da hallaka mutane takwas.

Mahaukaciyar iska da ruwan sama da ake yi a kasar Philippines
Mahaukaciyar iska da ruwan sama da ake yi a kasar Philippines Reuters
Talla

Yankin data dira dake arewacin tsubirin Luzom, ya kasance yanki ne dake da mutane akalla miliyan 10 wadanda yawanci ke zaune a gidaje da aka yi da katako.

Majiyoyin samun labarai sun ce,  yanzu haka a yankin  babu hasken wutan lantarki, itatuwa sai faduwa suke yi, a yayin da rufin gidaje ke kwarewa.

tuni dai kungiyar agaji ta Handicap International, ta aika da tawagar masu aikin jinkai domin taimakawa a kasar Philippines,  tare da yin kiran masu bada taimako, su taimakawa  al’umar da suka samu kansu cikin hali, sakamakon mahaukaciyar guguwar dake dauke da ruwan saman da ta  rutsa da su.

guguwar dai ta kasance mafi karfi dake gudun 255 a awa da ta shafi   tsibirin na Philippines  a wannan shekara.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.