Isa ga babban shafi
Amurka-Faransa

Trump ya ce yana sanya idanu kan zanga-zangar Faransa

Shugaban Amurka Donald Trump ya ce yana ci gaba da sa ido kan zanga zangar da ke gudana a Faransa, a wani yunkuri na sake fito da barakar da ke tsakaninsa da shugaba Emmanuel Macron.

Cikin sakon na Trump da ya wallafa a Twitter ya ce yana sane tare da sanya idanu a zanga-zangar wadda kuma ya zama wajibi shugaba Macron ya dauki matakan da suka dace.
Cikin sakon na Trump da ya wallafa a Twitter ya ce yana sane tare da sanya idanu a zanga-zangar wadda kuma ya zama wajibi shugaba Macron ya dauki matakan da suka dace. REUTERS/Leah Millis
Talla

A sakon da ya aike ta kafar twitter, Trump ya bayyana cewar zanga zangar da tashin hankalin da ake samu ba su da nasaba da yadda aka ci zarafin Amurka wajen yarjejeniyar kasuwanci da kasashen Turai da kuma biyan kudin tsaro domin kariya.

Trump ya ce ya zama dole a sake gyara wadannan batutuwa guda biyu cikin gaggawa.

Akalla mutane 130 aka kama bayan zanga zangar ranar asabar da ta haifar da tashin hankali.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.