Isa ga babban shafi

Tawagar ECOWAS ta sake komawa Nijar don ganawa da sojoji da suka yi juyin mulki

Tawagar Kungiyar kasashen Afirka ta Yamma, wato ECOWAS ta isa birnin Yammai na Jamhuriyar Nijar domin ganawa da sojojin da suka yi juyin mulki a kasar. Tawagar wadda ke karkashin jagorancin tsohon shugaban mulkin soji na Najeriya, Janar Abdusalami Abubakar, na kuma dauke da mai alfarma Sarkin Musulmin kasar, Muhammad Sa’ad Abubakar tare da wasu jami’an ECOWAS. 

Firaministan Nijar ya na mai ganawa da shugaban Tawagar Ecowas a Yammai,Janar Abdul Salami
Firaministan Nijar ya na mai ganawa da shugaban Tawagar Ecowas a Yammai,Janar Abdul Salami © Nigeria Presidency
Talla

Firaministan da sojoji suka nada Ali Muhammad Lamine Zeine ne ya karbi tawagar a filin jirgin saman Yammai bayan isarta kasar, yayin da rahotanni ke bayyana cewar ana saran ta gana da shugaban sojin da ya jagoranci juyin mulki, Janar Abderahmane Tchiane da kuma shugaba Bazoum Mohammed. 

Firaministan Nijar a lokacin da ya karbi tawagar Ecowas a filin tashi da saukar jirage a Yammai
Firaministan Nijar a lokacin da ya karbi tawagar Ecowas a filin tashi da saukar jirage a Yammai © Nigeria Presidency

Wannan ce ziyara ta biyu da wannan tawaga ta kai Nijar, bayan wadda ta kai a baya, wanda shugaban sojin yaki karbar su. 

Wannan ziyarar kuma tana zuwa ne kwana guda bayan kammala taron hafsoshin sojin kasashen Afirka ta Yamma wanda ya gudana a kasar Ghana. 

Firaministan Nijar ya na mai ganawa da shugaban Tawagar Ecowas a Yammai,Janar Abdul Salami
Firaministan Nijar ya na mai ganawa da shugaban Tawagar Ecowas a Yammai,Janar Abdul Salami © Nigeria Presidency

Hafsoshin sun ce sun kammala duk wani Shirin da ya dace domin mayar da mulkin farar hula a Nijar, abinda suke jira kawai shine umarni daga shugabannin kasashen wadanda ke ci gaba da daukar matakan diflomasiya domin ganin an kaucewa daukar matakin sojin. 

A ziyarar da malaman addinin Islama daga Najeriya suka kai a makon jiya, a karkashin jagorancin Sheikh Bala Lau, sojojin sun bayyana musu aniyar tattaunawa da ECOWAS da kuma bukatar ganin an cirewa kasar takunkumin karya tattalin arzikin da aka kakabawa Nijar. 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.