Isa ga babban shafi
Norway

Dan bindigar Norway ya amsa rashin laifi bayan ya gurfana gaban Kotu

Anders Behring Breivik wanda ya amsa bindige mutane 77 a kasar Norway a watan Juli zai gurfana gaban kotu a Oslo inda wasu ke ganin yana da tabin hankali.

Anders Behring Breivik Dan bindigar da ya kashe mutane 77 a kasar Norway
Anders Behring Breivik Dan bindigar da ya kashe mutane 77 a kasar Norway REUTERS/Lise Aserud/Scanpix Norway/File
Talla

A ranar 22 ga watan Yuli ne, Breivik, ya kashe mutane Takwas bayan dala wani bom a wata mota da aka ajiye a harabar ginin ofishin Jens Stoltenberg, Fira ministan kwadago.

Daga nan ne kuma Breivik ya je Tsibirin Utoeya bayan ya yi shiga ‘Yan Sanda ya bude wuta a gungun matasa da suka halarci wani bukin Jam’iyyar Labour.

Wani binciken likitoci ya nuna, lafiyar Dan ta’addan kalau lokacin da ya kai harin, kuma shima da bakinsa ya amsa cewa da lafiyar shi.

Mista Breivik yace ya kai harin ne domin adawar shi da yadda Musulmi ke kutsa kai a Turai.

 

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.